Kwamitin gwamnatin tarayya dake kula da yaki da cutar coronavirus ya bayyana cewa an sake aikawa jihohi kudade dan su yaki cutar coronavirus.
Shugaban kwamitin, Boss Mustapha ne ya bayyana haka a ganawa da manema labarai.
Yace an aikawa jihar Legas Biliyan 10 inda aka aikawa Kano Biliyan 5 sannan kuma an aikawa sauran jihohin Najeriya Biliyan 1 kowacce su yaki coronavirus.